in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Senegal ta amince da shigar da wasu jiragen sama da na ruwa daga kasashe masu fama da cutar Ebola a cikin kasar
2014-11-15 10:24:39 cri
Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Senegal ta bayar da sanarwa a ranar 14 ga wata, inda ta ce ta amince da shigar da wasu jiragen sama da na ruwa daga kasashen Guinea, Liberia da Saliyo a cikin kasar, amma za ta ci gaba da rufe iyakar kasa dake tsakaninta da kasar Guinea.

A sakamakon cutar Ebola da ta yi tsanani a yankin yammacin Afirka, kasar Senegal ta sanar da rufe iyakar kasa a tsakaninta da kasar Guinea a ranar 21 ga watan Agusta, kana ta hana shigar da jiragen sama da na ruwa daga kasashen Guinea, Saliyo da Liberia a cikin kasar.

A ranar 6 ga wannan wata, kungiyar ECOWAS ta gudanar da taron kolinta a birnin Accra dake kasar Ghana, inda ta yi kira ga kasashe membobin kungiyar da su kara sa ido kan iyakar kasa a fannin lafiyar jikin mutum, da soke matakan rufe iyakar kasa don tabbatar da yin zirga-zirgar mutane da kayayyaki a tsakanin kasashe membobin kungiyar. Yadda kasar Senegal ta amince da shigar da jiragen sama da na ruwa daga kasashe masu fama da cutar Ebola a cikin kasar, wannan ya nuna amsa kiran da kungiyar ECOWAS ta yi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China