in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a ci gaba da yin kokari wajen rigakafi da yaki da cutar Ebola
2014-11-14 10:22:39 cri
A jiya Alhamis 13 ga wata ne, shugaban shirin yaki da cutar Ebola na MDD Anthony Banbury ya bayyana cewa, ana samun babban ci gaba kan aikin yaki da cutar Ebola a fadin duniya, amma duk da haka ya zama wajibi a ci gaba da zage damtse wajen yin rigakafin cutar a unguwoyi, ta haka za a cimma nasara kan yaki da cutar.

Bisa labarin da jaridar Cameroon Tribune ta bayar, an ce, bisa kiran da kungiyar AU da bankin raya Afirka wato AFDB suka yi, shugabannin bangaren ciniki na kasashen Afirka sun gudanar da taro a birnin Addis Ababa dake kasar Habasha a kwanakin baya, inda suka tsaida kudurin kafa asusun yaki da cutar Ebola da zai bukaci dala miliyan 28.5 don tura likitoci a kalla dubu daya zuwa kasashen Guinea, Liberia da Saliyo inda za su bada jinya ga wadanda suka kamu da cutar Ebola. Kuma bankin AFDB ne zai tafiyar da harkokin asusun.

Ya zuwa yanzu, bankin AFDB ya bada kudi dala miliyan 223 don taimakawa wajen yaki da cutar Ebola. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China