A gun bikin rufe kwarya-kwaryar taron kungiyar APEC karo na 22 da aka yi a kwanakin baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi nuni da cewa, a yayin da ake kokarin fama da cutar Ebola dake yaduwa, shugabannin mambobin kungiyar APEC sun tsaida kudurin hadin gwiwarsu don taimakawa kasashen Afirka wajen tinkarar cutar da kuma shawo kanta, baya ga nuna goyon baya ga MDD da ta bada gudummawa ga kasashen Afirka da taka muhimmiyar rawa wajen yaki da cutar Ebola, da kuma bada taimako ga jama'ar dake yankuna masu fama da cutar Ebola don tinkarar cutar har zuwa lokacin da za a kawar da ita. (Zainab)