in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta habaka hadin gwiwar kimiyya da fasaha da cinikayyar noma da Afirka
2014-11-14 16:47:51 cri
Babban manajan kula da harkokin tattalin arziki na ma'aikatar harkokin noma na kasar Sin Qian Keming ya bayyana a yau Jumma'a 14 ga wata cewa, ma'aikatar na son karfafa mu'amalar ayyukan noma dake tsakaninta da hukummomin kasashen Afirka, kungiyar tarayyar kasashen Afirka, kungiyar abinci da ayyukan noma ta MDD da kuma kungiyar cinikayya ta duniya WTO da dai sauransu, don kafa da kuma kyautata tsarin hadin gwiwar ayyukan noma da karfafa cinikayyar hajojin hatsi dake tsakanin Sin da Afirka.

Qian Keming ya bayyana haka ne a yayin zaman tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka karo na biyar da ake yi a birnin Wanning na kasar Sin, a yau Jumma'a, yayin taron karawa juna sani kan hadin gwiwar aikin noma tsakanin Sin da Afirka, Mr. Qian ya yi bayani cewa, aikin noma shi ne tushen bunkasuwar zaman takewar al'umma, akwai isassun filayen noma da kuma hasken rana a nahiyar Afirka, lamarin da ya dace da raya aikin noma a Afirka sosai, kana kasar Sin na da fasahohin noma na zamani, shi ya sa hadin gwiwar Sin da Afirka kan harkokin noma ta dace da moriyar juna sosai, ta yadda za su iya kyautata harkokin noman bangarorin biyu bisa taimakon juna.

Ya kuma kara da cewa, ya zuwa yanzu, kasar Sin ta riga kulla yarjejeniyoyi da dama tare da kasashen Afirka guda 17 da wasu kungiyoyin da abin ya shafa, gaba daya ta ba da taimako wajen gina cibiyoyin fasahohin aikin noma guda 22 na gwaji, kana ta aike da manyan masanan aikin noma da dama zuwa Afirka, sannan ta horas da 'yan Afirka sama da dubu 5 kan harkokin tattalin arzikin noma da fasahohin noma a kasar Sin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China