in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta Kudu ta kaddamar da shirin bunkasa noma da tsaron abinci
2013-09-18 10:36:03 cri

Gwamnatin Afrika ta Kudu ta sanar a ranar Talata cewa, ta kaddamar da wani shirin kasa domin bunkasa noma da tsaron abinci, bisa kokarinta na kawar da talauci da yunwa. Kuma ana tafiyar da shirin a karkashin jagorancin ma'aikatar cigaban al'umma, a cewar ministar noma madam Tina Joemat-Petterson a yayin wani taron manema labarai a birnin Johannesburg. A cikin tsarin wannan shiri, manufar bunkasa noma ita ce neman filayen noma masu kyau da ba'a yawan amfani da su a cikin kasar da kuma za'a iyar amfani da su wajen samar da abinci, in ji ministar tare da jaddada muhimmancin noma wajen rage talauci, kuma a cikin wannan wata ne gwamnatin Afrika ta Kudu za ta ba da sanarwar bude lokacin yin shuke-shuke na shekarar 2013 zuwa ta 2014, ta yadda za'a iyar baiwa jama'a kwarin gwiwa na shuka kayayyakin lambu da hatsi a cikin gonakinsu. A karshen wannan shiri, wasu kayayyakin da aka noma za'a rarrabawa talakawa, yayin da sauran za'a shigar da su kasuwanni.

A lokacin da take bayyana niyyarta wajen yaki da talauci a Afrika ta Kudu, madam Joemat-Petterson ta nuna cewa, gwamnatin kasar ta yi imanin cewa, wannan shiri zai dauki babban matsayi wajen kawar da talauci da bunkasa tattalin arzikin yankunan kasar baki diya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China