in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata jami'ar AU ta nuna yabo da kokarin Sin na taimakawa ayyukan noma a Afrika
2014-01-29 10:40:14 cri
Kasar Sin ta nuna azama sosai domin bunkasa bangaren noma a nahiyar Afrika, in ji kwamishinar tarayyar Afrika kan tattalin arzikin karkara da noma, madam Tumusiime Rhoda Peace a ranar Talata.

A yayin wani taron manema labarai a ranar Talata a lokacin babban taron tarayyar Afrika karo na 22 a cibiyar kungiyar dake birnin Addis Ababa na kasar Habasha, kwamishinar ta nuna cewa kasar Sin ta taimakawa nahiyar Afrika sosai musamman ma a fannonin gine-gine, lamarin da ta bayar da muhimmancin gaske ga raya kasuwanci tsakanin kasashen Afrika da kuma bunkasa aikin noma a nahiyar.

Kasar Sin na daya daga cikin abokan huldar da kungiyar AU take fadada dangantaka a fannin noma, in ji madam Rhoda Peace.

Afrika na karuwa sosai daga kasar Sin musammun ma ta fuskar noma, bayan kuma tana taimakawa bunkasa gine-ginen ayyukan more rayuwa a yawancin kasashen Afrika, haka kuma kasar Sin tana zuba jari a cikin kamfannonin sarrafa albarkatun gona ta hanyar bangaren kamfannoni masu zaman kansu, in ji wannan jami'a. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China