in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Amurka sun jefa wa dakarun Kurdawa makamai daga sama don taimaka musu wajen yaki da kungiyar IS
2014-10-21 15:43:39 cri

Wata sabuwa kuma, an ce, babbar hedkwatar ba da umurni ga sojojin kasar Amurka ta ba da sanarwa a ran 20 ga wata cewa, sojojin kasar Amurka sun jefa makamai da kayayyakin jiyya daga sama ga dakarun Kurdawa da ke Ayn al-Arab, wani muhimmin garin dake arewacin kasar ta Sham, domin taimaka musu wajen yaki da 'yan tsattsauran ra'ayi na kungiyar IS.

Sanarwar kuma ta bayyana cewa, ya zuwa yanzu, kawancen yaki da kungiyar IS dake karkashin jagorantar kasar Amurka ya riga ya kai hare-haren sama kan garin Ayn al-Arab har sau 135, hakan ya hana kokarin da mayakan IS ke yi na shiga garin.

Dadin dadawa, an ba da labarin cewa, wani jami'in dakarun Kurdawa na kasar Sham ya bayyana a kwanan baya cewa, dakarunsa sun samu nasarar tsaron garin Ayn-al-Arab bisa taimakon da Amurka da sauran kasashe suka bayar kan kai farmaki daga sama. Da ma kungiyar IS ta mamaye yankunan garin kusan kashi 40 bisa 100 a baya, amma yanzu wannan adadi bai kai kashi 20 bisa dari ba. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China