in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rikicin da ya abku a Iraki ya haddasa mutuwar mutane fiye da 140
2014-09-29 14:14:00 cri
Bangaren soja na kasar Iraki ya bayyana a jiya Litinin cewa, rikici ya barke tsakanin sojojin kasar da kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi, ciki har da ISIS, wanda ya haddasa mutuwar wasu 'yan dakaru da sojojin tsaro sama da 140.

A wannan rana, shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya bayyana cewa, farmaki ta sama da kasar Amurka da kawayenta suka kai wa ISIS ba su iya kawar da kungiyar kwata-kwata ba. Saboda haka, kamata ya yi kasashen duniya su kara daukar matakan da suka dace, wato ba kawai a kai farmaki ta sama ba, har ma za a kaddamar da hari ta kasa. Shugaban ya kara da cewa, kasarsa za ta yi iyakacin kokarinta da nufin yaki da dukkan kungiyoyin ta'addanci na yankin.

A nasa bangaren ma, shugaba Barack Obama na kasar Amurka a cikin wata hira da aka watsa a tashar CBS a daren ranar 28 ga watan nan, ya amince da cewa, hukumomin leken asiri na kasarsa ba su zaci cewa, ISIS tana da karfi kamar haka ba, a waje guda kuma sun auna karfin sojojin Iraki fiye da kima. Sakamakon kuskuren hasashen da Amurka ta yi ne, yankin Gabas ta Tsakiya ya kasance masomin ISIS. A cewar Obama, daga karshe dai dole ne a warware rikicin Iraki da Syria a siyasance. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China