in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na MDD ya yi kira da a ba da kariya ga Kobane a Syria
2014-10-11 10:34:25 cri
Jiya ranar 10 ga watan nan, manzon musamman na MDD dake kula da batun Syria Staffan de Mistura ya yi kira ga kasashen duniya da su dauki matakai ba tare da bata lokaci ba, don hana kungiyar ISIS ta mamaye Kobane, muhimmin yanki dake arewacin kasar Syria.

Mistura wanda ya bayyana haka a yayin taron manema labaru da aka shirya a Geneva, ya yi gargadin cewa, yanzu yankin Kobane na cikin yanayi mai tsanani, sakamakon harin da kungiyar ISIS ke yi, idan kungiyar ta mamaye yankin, to mai yiwuwa ne za ta yi kisan gilla kan mutanen dake zama a wurin, da kuma wadanda ke yankunan dake dab da Kobane.

Mistura ya kara bayyana cewa, kamata ya yi, kasa da kasa su dauki matakan da suka dace bisa tushen girmama dokokin duniya, da mulkin kai da cikakken yankin kasar Syria don hana abkuwar irin masifa mai bakin ciki. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China