in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu ya la'anci jerin farmakin da kungiyar IS ta kai
2014-10-18 16:40:20 cri
A daren jiya ranar 17 ga watan nan, kwamitin sulhu na MDD ya bayar da sanarwa ta kafofin watsa labaru, inda ya la'anci jerin farmakin da kungiya mai tsattsauran ra'ayi ta IS ta kai a kwanan baya, ya kuma jaddada cewa, akwai wajibin murkushe wannan kungiya.

A cikin sanarwar an ce, a 'yan kwanakin da suka wuce, kungiyar IS ta tayar da jerin farmaki a Bagadaza, babban birnin kasar Iraki, da kuma jihohi da lardunan dake kewayensa, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutanen Iraki fiye da 10. Kwamitin sulhun ma ya yi zargi sosai kansu tare da jaddada cewa, za a gudanar da bincike kan wadanda suka keta dokokin jin kai na duniya, da take hakkin bil Adama a cikin kasar Iraki.

Haka zalika kwamitin sulhu ya sake nanata a cikin sanarwar cewa, dole ne za a cimma nasarar yaki da kungiyar IS, kuma akwai bukatar a yi namijin kokari don murkushe ayyukan ta'addanci bisa abubuwan da aka tanada cikin tsarin dokoki na MDD, kana da kawar da barazanar da suke kawowa zaman lafiya da tsaron duniya. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China