in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ISIS tana shirin kai kari kan jirgi mai tafiya a karkashin kasa na Amurka da Faransa
2014-09-26 11:13:47 cri
Firaministan kasar ta Iraqi Haider Al-Abad ya halarci taron da aka yi a cibiyar MDD dake birnin New York a ran 25 ga wata, inda ya bayyana cewa, kungiyar ta'addanci ta ISIS tana shirin kai hari kan jirgi mai tafiya a karkashin kasa na Amurka da Faransa.

A cewarsa, hukumar leken asiri ta kasar Amurka ta sami wasu abubuwan dake cikin bayyanai daga mambobin ISIS da aka tsare.

Jami'in mai kula da aikin yaki da ta'adanci na ofishin 'yan sandan birnin New York John Miller ya sanar da yin bincike kan lamarin bayan da ya samu gargadin da Al-Adad ya bayar.

A nata bangare kuma, fadar shugaban kasar Faransa ta ba da sanarwa a ran 25 ga wata cewa, shugaban kasar François Hollande ya halarci taron tsaron kasar da aka yi a wannan rana, inda ya yanke shawarar kara daukar matakai a wasu wuraren jama'a na kasar domin tinkarar ayyukan ta'adda.

Ban da haka kuma, shugaban kasar Iran Hassan Rouhani wanda ke halartar babban taron MDD ya bayyana a wannan rana na 25 ga wata cewa, dalilin tasowar kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi, ciki hadda ISIS shi ne, tsari na kuskure da kasashen yamma ke dauka a yankin gabas ta tsakiya da dai sauran yankuna, don haka ya kamata kasashen duniya su hada kai a tinkare su. Kuma ya kamata a gano a kuma kawar da tushensu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China