in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Obama da Ban Ki-moon sun tattauna game da kafa kawancen kasa da kasa wajen yaki da kungiyar ISIS
2014-09-09 15:38:28 cri
Fadar shugaban kasar Amurka ta White House ta fidda wata sanarwa dake cewa, shugaban kasar Barack Obama ya zanta da babban magatakardar MDD Ban Ki-moon da firaministan kasar Australia Tony Abbott ta wayar tarho, inda suka tattauna game da kudurin kafa kawancen kasa da kasa domin yaki da kungiyar ISIS mai rajin kafa kasar Musulunci.

Cikin sanarwar, fadar shugaban kasar Amurka ta bayyana cewa, Obama da Ban Ki-moon sun yi imani cewa, akwai bukatar kafa wani kawance na kasa da kasa, domin yaki da kungiyar ta ISIS, kana sun yi alkawarin ci gaba da bada gudummawar jin kai, ga fararen hula na kasar Iraki da ke fuskantar barazanar kungiyar ta ISIS. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China