in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta shigar da sunayen wasu membobin kungiyar ISIS da ta Al-Qeada a cikin jerin sunayen mutanen da aka kakabawa takunkumi
2014-09-25 15:30:48 cri

A ranar 24 ga wata, shugaban kasar Amurka Barack Obama ya yi kira ga kasa da kasa da su kulla kawancen da Amurka take jagoranci wajen yaki da kungiyar ISIS. Kana ma'aikatar harkokin wajen kasar ta bayar da sanarwa a wannan rana cewa, kasarta ta mai da mambobin kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi guda goma a matsayin 'yan ta'adda na duniya. Don haka Amurka za ta hana su yin amfani da kudin ta kamar yadda dokokin shari'ar kasar ta tanada.

A yayin da Obama yake yin jawabi a gun babban taron MDD a wannan rana, ya bayyana cewa, kungiyar ISIS ta aikata manyan laifuffuka da dama a yankunan kasar Iraki da na Syria. Ya ce, kasar Amurka za ta murkushe wannan kungiya ta hanyar kafa kawancen yaki da ita.

Kamar yadda ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta jaddada a ranar 24 ga wata cewa, harin saman da kasar Amurka ta kai ga 'yan ta'addan a kasar Syria ba ya bisa doka, don haka ta yi kira ga kasa da kasa dake dauke nauyin kansu da su tsara manufofin yaki da ta'addanci tare.

Hukumar watsa labaru ta shugaban kasar Rasha ta bayar da sanarwa a ranar 23 ga wata, cewa shugaban kasar Vładimir Putin ya buga wayar tarho ga babban Magatakardar MDD Ban Ki-moon don tattauna kan batun yaki da kungiyar ta'addanci, inda ya jaddada cewa, bai kamata ba a kai harin sama ga kungiyar ISIS a kasar Syria ba tare da samun izni daga gwamnatin kasar Syria ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China