in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka da kasashen Larabawa 10 sun amince da yaki da kungiyar ISIS tare
2014-09-12 15:19:38 cri
Jiya Alhamis 11 ga wata, sakataren harkokin waje na Amurka John Kerry ya yi taro da ministocin kasashen Larabawa 10 a birnin Jeddah dake yammacin kasar Saudiya, inda aka ba da sanarwar cewa, Amurka da wadannan kasashen Larabawa 10 sun amince da yaki da duk kungiyoyin ta'addanci tare, ciki da akwai kungiyar ISIS, domin kafa wata hadaddiyar kungiyar yaki da ISIS a duk fannoni.

Sanarwar ta ce, wadannan kasashe sun amince da hana dakaru masu tsattsauran ra'ayi da su shiga Syria ko Irak daga kasashen makwabta, da yaki da aikin zuba jari ga kungiyar ISIS da sauran kungiyoyin ta'addanci, a kokarin cafke su bisa dokoki.

Dadin dadawa, kasashen sun amince da ba da taimakon jin kai ga yankunan dake fama da ayyukan ta'addanci, domin ba da taimako wajen samun farfadowa, da nuna goyon baya ga kasashen dake yin gwagwarmaya da kungiyoyin ta'addanci.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China