in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya nuna maraba game da kokarin gamayyar kasa da kasa wajen yaki da cutar Ebola
2014-09-13 17:05:24 cri
Jiya Jumma'a 12 ga wata, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya ba da wata sanarwa, inda ya nuna yabo game da kokarin gwamnatin kasar Cuba wajen tura ma'aikatan kiwon lafiya 165 zuwa kasar Saliyo, da na gamayyar kasa da kasa kan ba da taimako domin hana yaduwar cutar Ebola, haka kuma, ya yi kira ga karin kasashen duniya da kungiyoyi da su ba da taimako kan lamarin.

A yayin da kakakin babban magatakardan MDD Stephane Dujarric ya gabatar da wannan sanarwa, ya ce, a halin yanzu, domin yaki da cutar Ebola, kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU tana kokarin tura likitoci zuwa kasashen dake fama da cutar, haka kuma, ana ci gaba da samun taimakon kudade, kayayyakin agaji da masanan kiwon lafiya daga kasa da kasa, kungiyoyi da kuma kamfanoni masu zaman kansu suka samar.

Bugu da kari, cikin sanarwar, Mr. Ban ya nuna maraba ga kasashen Burtaniya da Amurka da suka tura masanan kiwon lafiya zuwa yammacin kasashen Afirka, da kuma gina cibiyar agaji a kasashen, ya kuma yi kira ga karin hukumomin kasa da kasa da su dauki matakai cikin sauri don samar wa kasashen dake fama da cutar Ebola taimako yadda ya kamata.

A sa'i daya kuma, Mr. Ban ya yi kira ga kasashen da abin ya shafa da kada su rufe iyakokinsu da kasashen Guinea, Saliyo da dai sauran kasashen da cutar Ebola ta shafa, haka kuma, ya kamata a tabbatar da amfanin hanyoyin sama da na kasa wajen shiga kasashen dake bukatar taimako. Sabo da matakin rufe hanyoyin zai haifar da karin barazana, da ja da bayan ayyukan hana yaduwa da yin rigakafi kan cutar Ebola. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China