in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kara ba da sabon tallafin yakar cutar Ebola
2014-09-12 21:00:42 cri
A yau ne kasar Sin ta bayyana karin tallafin jin kai ga kasashen Afirka da kungiyoyin kasa da kasa na Yuan miliyan 200 kimanin dala miliyan 32.54 don taimaka wa wajen yaki da cutar Ebola.

Wata sanarwa da ma'aikatar cinikayya ta Sin ta bayar, ta ce tallafin zai hada da abinci, kayayyakin hana yaduwar cututtuka, kayayyakin rigakafin ko-ta-kwana da tallafin jari.

Bugu da kari kasar ta Sin za ta karfafa wani hadin gwiwar kiwon lafiya da kasashen Afirka na dogon lokaci, don agaza musu wajen inganta karfin hanyoyinsu na kare yaduwar cututtuka da kuma inganta tsarinsu na kiwon lafiya.

Ko da a watan da ya gabata, Sin ta baiwa kasashen na Afirka tallafin jin kai na Yuan miliyan 30.

A cewar hukumar lafiya ta duniya mutane 4,268 ne suka kamu da cutar ta Ebola yayin da mutane 2,288 suka mutu a kasashen Guinea, Liberia, Saliyo da Najeriya sanadiyar cutar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China