in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wanda ya kamu da cutar Ebola a Senegal ya warke
2014-09-11 15:58:21 cri
Rahotanni daga kasar Senegal na cewa sakamakon binciken baya bayan nan da aka gudanar kan dalibin nan mai shekaru 21 da haihuwa wanda ya kamu da cutar Ebola, ya nuna cewa yanzu haka ya warke sarai.

A ranar 29 ga watan Agustar da ya shude ne dai mahukuntan kasar ta Senegal suka bayyana wannan matashi dan asalin kasar Guinea, a matsayin mutum na farko da ke dauke da cutar Ebola da aka gano a kasar, tun barkewar ta a wasu kasashen yammacin Afirka a watan Fabrairun bana.

Wannan matashi dai ya shiga kasar Senegal ne daga kasar Guinea tun kafin an rufe iyakar kasashen biyu, kuma kafin hakan an ce ya yi cudanya da wadanda suka kamu da cutar Ebola a Guinea.

Bayan da hukumar kiwon lafiyar kasar Senegal ta gano hakan ne aka fara yi masa magani, a wani wuri da aka kebe domin hana yaduwar cutar, aka kuma killace wadanda suka yi cudanya da shi bayan shigar sa kasar su 67. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China