in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 35 sun rasu a Congo Kinshasa sakamakon kamuwa da cutar Ebola
2014-09-10 14:24:33 cri
Wani jami'i a ma'aikatar kiwon lafiyar kasar Congo Kinshasa, ya bayyana wa 'yan jarida a jiya Talata cewa, tuni mutane 35 a kasar sun rasa rayukansu sakamakon kamuwa da cutar Ebola, yayin da kuma wasu karin mutane 14 ke dauke da cutar a halin yanzu.

Ya ce dukkanin mutanen da suka mutu ko aka tabbatar sun kamu da cutar suna zaune ne a yankin Gera dake jihar Equateur ta kasar.

Tun dai ranar 2 ga watan nan na Satumba ne hukumar kiwon lafiya ta duniya, ta bayar da wata sanarwa dake tabbatar da bullar cutar Ebola a kasar ta Congo Kinshasa, ko da yake an ce hakan ba shi da nasaba da yaduwa cutar, a wasu kasashen dake yammacin Afirka a halin yanzu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China