in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Isra'ila ta mai da martani kan harin da Falesdinu ta kai mata
2014-08-20 10:22:25 cri

Bangaren sojojin tsaron kasar Isra'ila ya ba da wata sanarwa a ran 19 ga wata, inda ya nuna cewa, a wannan rana da yamma, sojojin kasar sun kai hare-haren sama sau biyu kan yankin Gaza, don mai ta martani ga makaman rokar da dakarun Hamas dake yankin Gaza suka harba musu. Haka kuma, bisa labarin da aka samu, an ce, ya zuwa yanzu, hare-haren da Isra'ila ta kai ta sama sun haddasa mutuwar mutane guda 3, yayin da sama da mutane 40 suka jikkata.

Wani jami'in Falesdinu ya bayyana cewa, ba a samu ci gaba ba kan shawarwarin tsagaita bude wuta cikin dogon lokaci da ke tsakanin Isra'ila da Falesdinu.

Bayan aka kawo karshen yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta sa'o'i 120 a daren ranar 18 ga wata, Isra'ila da Falesdinu ba su iya cimma daidaito kan tsagaita bude wuta cikin dogon lokaci ba, illa kawai sun yarda da tsawaita wa'adin yarjejeniyar zuwa daren ranar 19. Sai dai rikicin ya sake barkewa a yammacin ranar 19, lamarin da ya kawo karshen yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

Bugu da kari, bambancin ra'ayi da ke tsakanin bangarorin biyu ya janyo cikas ga shawarwarin neman cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta cikin dogon lokaci, wadanda a halin yanzu, kasar Masar ke kokarin shiga tsakani a kai. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China