in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan Falesdinu da Isra'ila za su ciyar da shawarwarin zaman lafiya tsakaninsu
2014-01-21 16:40:27 cri
A ran 20 ga wata, zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Liu Jieyi ya bayyana cewa, a halin yanzu, ana cikin wani muhimmin mataki na shawarwarin zaman lafiyar tsakanin Falesdinu da Isra'ila, kuma kasar Sin tana fatan bangarorin biyu za su yi amfani da wannan dama wajen aza harsashin da zai samar da sakamako mai gamsuwa tun da wuri bisa shawarwarin zaman lafiya dake tsakaninsu.

A wannan rana, kwamitin sulhu na MDD ya kira wani taro a fili dangane da batun Gabas ta Tsakiya, inda Liu Jieyi ya bayyana cewa, kasar Sin na goyon bayan shawarwarin zaman lafiya da ake yi a halin yanzu tsakanin Falesdinu da Isra'ila, kuma abu mafi muhimmanci ga shawarwarin dake tsakaninsu shi ne, bangarorin biyu su amince da ikon juna, tare da nuna fahimtar juna.

Ya ce, a halin yanzu dai, ya kamata a dakatar da gina matsugunan Yahudawa, kawo karshen tashe-tashen hankali da kuma kawar da duk wani hani da aka yi wa yankin Gaza daga dukkan fannoni, ta yadda za a iyar samun ci gaban shawarwarin.

Haka zalika, mista Jieyi ya kara da cewa, ya kamata gamayyar kasa da kasa ta dukufa wajen ciyar da shawarwarin zaman lafiyar tsakanin bangarorin biyu gaba, don kiyaye yanayin tsaro da na karko a yankin Gabas ta Tsakiya. Kasar Sin na fatan bangarorin hudu da batun Gabas ta Tsakiya ya shafa, wato MDD, kasar Amurka, kungiyar tarayyar kasashen Turai da kuma kasar Rasha za su dauki matakai yadda ya kamata don ciyar da shawarwarin gaba. Kasar Sin ta kuma nuna goyon baya ga kwamitin sulhu na MDD da ya ci gaba da ba da taimako kan wannan batun.

Bugu da kari, ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da dukufa wajen ciyar da shawarwarin zaman lafiya tsakanin Falesdinu da Isra'ila gaba bisa ra'ayoyi guda hudu da shugaban kasar Xi Jinping ya gabatar, don ba da gudummawa wajen shimfida zaman lafiya daga duk fannoni a yankin Gabas ta Tsakiya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China