in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Isra'ila ta amince da tsawaita wa'adin tsagaita bude wuta
2014-08-07 15:53:53 cri
A jiya Laraba 6 ga wata ne, wani jami'in kasar Isra'ila ya tabbatar da cewa, kasar Isra'ila ta amince da tsawaita wa'adin tsagaita bude wuta, kuma ana sa ran matakin zai iya kawo karshen hare-hare na wata guda da sojojin Isra'ila suka kaddamar kan yankunan al'ummar Falasdinawa, bisa abin da suka kira kiyaye tsaron iyakar kasar Isra'ila. Amma ya zuwa yanzu, kungiyar Hamas ta Palasdinu ba ta bayyana ra'ayinta kan lamarin ba.

Ko da yake jami'in ya bayyana aniyar kasar Isra'ila ta tsagaita bude wuta, amma bai yi karin bayani kan tsawon lokacin wa'adin ba.

A ranar 5 ga watan nan da karfe 8 na safe ne Palasdinu da Isra'ila suka fara aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta sa'o'i 72, sa'an nan bangarorin biyu suka aike da manyan wakilansu zuwa birnin Alkahira na kasar Masar don tattaunawa bisa shiga tsakanin kasar Masar, da nufin kulla wata yarjejeniyar dakatar da bude wuta cikin dogon lokaci.

Amma a daren jiya kakakin kungiyar Hamas ya musanta labarin tsawaita wa'adin tsagaita bude wuta cikin wata sanarwar da kungiyar ta fitar, inda ta ce, ba a tattauna kan batun tsawaita wa'adin tsagaita bude wuta ba a yayin shawarwarin da suka yi a birnin Alkahira.

Kaza lika, kamfanin dillancin labaran Masar na MENA ya ruwaito shugaban tawagar wakilan Falesdinu Azzam al-Ahmad wanda a halin yanzu ke birnin Alkahira na cewa, ya zuwa yanzu, ba a samu labarin cewa za a tsawaita wa'adin tsagaita bude wuta ba, amma akwai lokacin yin shawarwari kan wannan shiri kafin a kawo karshen wa'adin tsagaita bude wuta ta sa'o'i 72 da za ta kare a safiyar ranar 8 ga wata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China