in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gamayyar kasa da kasa sun amince da ra'ayin kasar Sin kan batun Falesdinu da Isra'ila
2014-01-09 16:59:36 cri
Kwanan baya, yayin da ya ke tsokaci kan ka'idoji hudu da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar dangane da shirin wanzar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana cewa, Falesdinu, Isra'ila da kuma gamayyar kasa da kasa sun amince da wadannan ka'idojin sosai, sabo da ka'idojin sun shafi fannonin daban daban da abin ya shafa.

Mr. Wang ya kuma bayyana cewa, ra'ayin kasar Sin kan batun Isra'ila da Falesdinu shi ne, bangarorin biyu su shata iyakokinsu bisa iyakar da aka tsara a shekarar 1967, ta yadda gabashin birnin kudus zai kasance babban birnin kasar, Falesdinu ta kasance kasa mai 'yancin kai, sa'an nan kuma a sami zaman lafiya tsakanin kasar Isra'ila da kasar Falesdinu, haka kuma, za a tabbatar da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya. Kasar Sin za ta ci gaba da dukufa don cimma wannan buri. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China