in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wurare da dama sun yi bukukuwan cika shekaru 77 da aukuwar yakin kin harin Japan
2014-07-07 21:44:24 cri

A ranar 7 ga watan Yuli wannan shekarar aka cika shekaru 77 da tuna da aukuwar yakin kin harin Japan a kasar Sin. A wannan rana, jama'ar wurare da dama na kasar sun yi bukukuwa, domin hana a manta da wannan abu da bayyana muhimmancin zaman lafiya.

A birnin Beijing, mutane da dama sun yi bukukuwa fiye da 40, da zummar tuna wannan rana na bakin ciki a tarihi da kuma saka kishin kasa a zukatan al'umma.

Wakilai kimanin 100 daga kungiyoyi daban-daban na yankin Hong kong sun yi zanga-zanga a kofar ofishin jakadancin kasar Japan dake Hong kong domin bayyana rashin jin dadinsu na shawarar da Japan ta yanke na maido da ikon daukar matakan soji, da gyara abubuwan dake cikin litattafan tarihi na makarantu yadda ta ga dama, da mamaye tsibirin Diaoyu na kasar Sin, inda suka nemi gwamnatin Japan da ta amince da gaskiyar laifukan da ta aikata da rogon gafara daga kasashen da ta taba kai ma hari. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China