in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin dake Senegal ya sake rubuta wani sharhi game da laifin Shinzo Abe
2014-01-29 20:37:25 cri
Kwanan baya, jakadan kasar Sin dake kasar Senegal Xia Huang ya sake rubuta wani sharhi, inda ya yi allah wadai da gwamantin Shinzo Abe na Japan dangane da abubuwan da ta aikata da kuma maganganun da ta yi wadanda ba su dace ba a cikin 'yan kwanakin nan, ya kuma yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su mai da hankali kan lamarin.

Cikin sharhinsa, Mr. Xia ya bayyana cewa, har yanzu, gwamnatin Shinzo Abe ba ta amsa laifuffukan da kasar ta aikata cikin tarihi ba, inda ta sha ta kai ziyara wurin ibadar Yasukuni da ake takaddama a kai, da ta kebe kaburburan masu laifukan yaki, ciki hadda wadanda suka jagoranci dakarun kasar yayin yakin duniya na biyu, lamarin da ya bata ran jama'ar kasar Sin sosai, wanda kuma ya kawo barazana ga dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

Mr. Xia ya kara da cewa, a halin yanzu, kasar Japan ita ce kasa mai samun bunkawuwar tattalin arziki, ana iya fahimta cewa, kasar tana da wani buri na siyasa, amma, idan tana son daukar alhakin shimfida zaman lafiya da na karko na kasa da kasa, ya kamata ta samu amincewar gamayyar kasa da kasa, musamman ma kasashen dake makwabtaka da ita. Kana, a halin yanzu, gwamnatin kasar Japan dake karkashin jagorancin Shinzo Abe na kokarin musanta bayanan tarihi, wannan zai haddasa illa ga kasarta, kuma ya kamata gamayyar kasa da kasa su mai da hankali kan wannan batu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China