in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata kasar Amurka ta kasance ba ta goyi bayan kowa kan batun tsibirin Diaoyu ba, in ji jakadan kasar Sin
2013-05-18 16:34:45 cri
Cui Tiankai, jakadan kasar Sin dake kasar Amurka, ya amsa tambayoyin wakilin mujallar 'Foreign Affairs' ta kasar Amurka, wadda ta buga zancen jakadan a shafin yanar gizonta a Jumma'a 17 ga wata, inda Cui ya nuna cewa, yanayin batun tsibirin Diaoyu ya kara tsanani ne sakamakon aikace-aikacen kasar Japan. Kamata ya yi kasashen Sin da Japan su tattana sosai don warware batun. Sa'an nan kasar Sin na son ganin Amurka ta kasance ba ta goyi bayan kowa a kan wannan batu ba.

Cui Tiankai ya ce, tsibirin Diaoyu da sauran kananan tsibiran dake kusa da shi sun kasance cikin yankin kasar Sin tun fil azal, saboda haka kasar Sin ba zata taba sauya ra'ayinta ba kan mallakar tsibirin, wanda a ganinta bai kamata a rika tuhumar hakan ba. Yayin da kasashen Sin da Japan suka yi kokarin kyautata huldar dake tsakaninsu, shugabannin kasashen 2 sun tsai da cewa za'a dakatar da ja'in ja a kan wannan batu. Sai dai tabarbarewar yanayin da aka shiga yanzu an same shi ne sakamakon aikace-aikacen kasar Japan.

Haka kuma a lokacin da ya tabo maganar zirin Koriya, Cui ya ce, kasar Sin tana tsayawa kan manufofi 3, wato da farko, tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a zirin Koriya. Na biyu, kokarin kau da makaman nukiliya a zirin. Sannan na uku ita ce, tsayawa kan hanyar tattaunawa don warware rikici. Wadannan manufofi 3 suna da alaka da juna, don haka kada a raba su. Kasar Sin, a nata bangaren, za ta ci gaba da kokari ganin an wanzar da zaman lafiya a zirin Koroya da kau da makaman nukiliya daga zirin. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China