in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta tinkari duk wani tada zaune tsaye da kasashen waje suka yi mata
2013-10-22 17:45:23 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a gun taron manema labaru da aka yi a yau Talata 22 ga wata cewa, kasar Japan ta dade tana ta da zaune tsaye, kana ta kara samun makamai, kasa da kasa sun nuna damuwa ga wannan yunkuri nata. Hua ta ce, Kasar Sin za ta tinkari duk wani yunkuri na ta da zaune tsaye da kasashen waje suka yi mata.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, gwamnatin kasar Japan ta tabbatar da shirinta na kakkabo jiragen saman da babu matuka da suka shiga sararin saman kasarta ba izni ba, ciki har da matakin harbo duk wasu jiragen saman da suke keta yankinta. A kwanakin baya, firaministan kasar Japan Shinzo Abe ya saurari rahoto game da wannan shiri, kuma ya amince da shi.

Game da wannan batu, Hua ta ce, kasar Japan ta ba da labari dangane da barazana daga kasashen waje, da yin amfani da wannan dalili don ta da zaune tsaye da kuma kara jibge makamai, kasa da kasa sun nuna damuwa sosai ga hakikanin yunkurinta.

Ban da wannan kuma, Hua ta jaddada cewa, tsibirin Diaoyu yankin kasar Sin ne, kasar Sin tana da karfi wajen tabbatar da ikon mallakar yankinta, kuma za ta tinkari duk wani ta da zaune tsaye da kasashen waje za su yi mata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China