in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar kasar Sin ta yi adawa da bukatar takwararta ta kasar Japan kan yankin tsaron sararin samaniya na kasar Sin
2013-12-08 17:01:37 cri
Kwamitin kula da harkokin waje na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya ba da sanarwa a ranar Asabar 7 ga wata, inda ya ba da amsa ga bukatar majalisar wakilai ta kasar Japan ta nemi kasar Sin da ta soke yankin tsaron sararin samaniya na tekun gabas na kasar.

Sanarwar ta ce yadda kasar Sin ta shata wannan yanki na tsaron sararin samaniya ya dace da dokokin kasa da kasa, don haka bai kamata kasar Japan ta yi korafe-korafe kan batun ba. Sa'an nan majalisar wakilan jama'ar kasar Sin sam ba za ta yarda da shirin kudurin da takwararta ta kasar Japan ta zartas dangane da batun ba.

Ban da haka, kwamitin ya nanata cewa, tsibirin Diao Yu da sauran kananan tsibiran dake kewayensa sun kasance cikin harabar kasar Sin tun fil azal, don haka ba wanda ke iya musunta ikon kasar Sin wajen mallakar tsibiran. Amma duk da haka kasar Japan ta sanya tsibirin Diao Yu cikin yankin tsaron sararin samaniya nata, abin da kasar Sin ba ta amince da shi ba ko kadan.

A karshen sanarwar, an bayyana cewa, matakan da kasar Japan ta dauka su ne ainihin sabani da halin kiki-kaka a yankin tekun gabas na kasar Sin. Don haka, an bukaci bangaren Japan da ta dakatar da matakan tsokana, don amfanawa kokarin kyautata huldar dake tsakanin bangarorin 2, da kiyaye kwanciyar hankali a yankin tekun gabas na kasar Sin. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China