in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in ma'aikatar harkokin wajen Sin ya gana da jakadun Amurka da Japan dake nan kasar Sin
2014-04-25 21:31:02 cri
A yammacin jumma'an nan wani babban jami'in ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya gana da jakadun kasashen Amurka da Japan dake nan kasar Sin. A lokacin ganawar da dukkan jakadun biyu daban daban ya nuna rashin jin dadin kasar Sin kan bayanin bayan taron da shugabbin kasashensu suka fitar sakamakon ziyara shugaba Obama a Japan.

Kasar Sin ta nuna rashin jin dadinta kan wasu abubuwan da ke cikin sanarwar da kasashen Amurka da Japan suka bayar cikin hadin gwiwa, in ji kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Qin Gang yau ranar Jumma'a 25 ga wata.

Qin Gang ya bayyana haka ne a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing, inda ya ce, yin soke-soke kan wasu kasashe bisa ga wasu batutuwa ba zai taimaka wajen warware batutuwa masu muhimmanci da kuma tabbatar da kwanciyar hankali a shiyya-shiyya ba.

A yau ne Amurka da Japan suka ba da wata sanarwar hadin gwiwa, inda Amurka ta ce, za ta tabbatar da tsaron yankunan kawarta Japan baki daya, ciki had da tsibirin Diaoyu, sa'an nan sun bayyana ra'ayoyinsu kan wasu batutuwan da suka shafi tekun gabashin kasar Sin da na kudancin kasar Sin.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China