in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Daliban kasar Ghana kimanin 100 za su fara karatu a kasar Sin
2013-08-28 14:05:16 cri
A ranar 27 ga wata, jakadan kasar Sin da ke kasar Ghana Gong Jianzhong ya bayyana cewa, daliban kasar Ghana su kimanin 111 sun samu kudin bonas daga gwamnatin kasar Sin, kuma za su fara karatu a kasar ta Sin tun daga watan Satumbar bana a zangon karatu na shekarar 2013 zuwa shekarar 2014.

A gun bikin ban kwana da aka shirya ga wadannan dalibai, Gong Jianzhong ya ce, hadin gwiwa a fannin ilmi ya zama wani muhimmin bangare na dangantakar hadin gwiwa da ke tsakanin kasashen Sin da Ghana, kuma kasar Sin tana fatan taimakawa kasar Ghana don ta samu bunkasuwa, ta hanyar horar da kwararru, da samar mata da fasahohi. Jakadan Gong ya yi fatan daliban kasar Ghana za su amfani wannan dama ta karatu a kasar Sin, su kuma kammala karatu cikin tsanaki, tare da kara fahimtar zamantakewar al'umma ta kasar, bayan da suka koma gida. Har ila yau ya yi fatan za su yi kokarin raya zamantakewar al'umma, da tattalin arzikin kasar ta Ghana, da kara sada zumunta ta gargajiya a tsakanin kasashen biyu.

A cikin jawabin da matar shugaban kasar Ghana Lordina Mahama ta yi, ta bayyana cewa, kasashen Ghana da Sin, na da dankon zumunci a tsakaninsu, a tsohon lokaci. Ta ce, kasar Sin ta taimakawa kasar Ghana wajen samar da muhimman ababen more rayuwa, da fannin ilmi, da kimiyya da fasaha da sauranu. Ta kuma yi kira ga daliban kasar ta Ghana, da su kiyaye dokokin kasar Sin, da girmama al'adun kasar, don kara ba da gudummawa wajen inganta hadin gwiwa da ke tsakanin kasashen biyu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China