in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar 'yan sanda ta Ghana ta shirya sosai domin fuskantar rikicin da ka iya barkewa a sakamakon zaben kasar
2013-08-02 15:02:15 cri
A ranar 1 ga wata, kakakin bangaren 'yan sanda na kasar Ghana Cephas Arthur ya bayyana cewa, 'yan sanda na kasar Ghana a shirye suke, don warware rikicin da ka iya bullowa sakamakon hukuncin da babbar kotun za ta yanke game da babban zaben kasar.

Arthur ya kuma yin kira ga bangaren da abin ya shafa da su kiyaye zaman lafiya na kasar, a kaucewa jawabin da zai haifar da tashe-tashen hankali.

Bayan babban zaben da aka gudanar a cikin watan Disamban bara a kasar Ghana, hukumar zabe ta sanar da cewa, shugaba mai ci na lokacin, John Dramani Mahama ya ci zaben, sai dai babbar jam'iyyar hamayya ta kasar NPP ta ce, an tabka magudi tare da watsi sakamakon wannan zabe, kuma ta kai kara ga babbar kotun kasar. Babbar kotun kasar ta yanke shawara cewa, a ranar 7 ga watan Agusta, za a yi wani zaman bahasi, inda kuma ake hasashen cewa, za a yanke hukunci na karshe nan ba da dadewa ba.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China