in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukunin aiki na Sin ya isa kasar Ghana
2013-06-12 16:23:33 cri
A ranar Talata 11 ga wata, rukunin aiki da ma'aikatar harkokin waje da ta cinikayya da kuma hukumar 'yan sanda ta Sin suka kafa, ya isa kasar Ghana, domin taimakawa ofishin jakadancin Sin a kasar wajen daidaita batun komawar gida ta Sinawa da aka kama bisa tuhumar su da hakar ma'adinin zinariya ba bisa doka ba .

A wannan rana, mambobin rukunin sun gana da shugabannin hukumar tsaron kasa da ta shige da fice ta Ghana, inda suka yi shawarwari kan batun yaki da hakar ma'adinin zinari ba bisa doka ba a wurin da kiyaye iko da moriyar Sinawa a wurin da sauransu.

Rukunin ya ce, gwamnatin Sin ta fahimta tare da girmama aikin da Ghana ta yi na yaki da hakar ma'adinin zinari ba bisa doka ba, da fatan daukar kwararran matakai tare da Ghana, a kokarin daidaita matsaloli yadda ya kamata. A don haka Sin ta bukaci Ghana da ta gudanar da bincike bisa dokoki yadda ya kamata, da dakatar da kame Sinawa a waje da yankunan hakar ma'adinai, da dakatar da ayyukan harin da wasu mutanen wurin suke kai wa Sinawan tare da kwace masu dukiyoyi, da kuma tabbatar da tsaron Sinawa da suke son komawa gida Sin, da kiyaye na'urori da sauran dukiyoyin Sinawa bisa iyakacin kokari da sauransu.

Wani jami'in gwamnatin Ghana ya ce, kasar na fatan karfafa mu'amala da hadin gwiwa tsakanin ta da kasar Sin, a kokarin daidaita batun yadda ya kamata. Kuma kasar za ta yi kokarin biyan bukatun Sin a fannoni daban daban.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China