in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na goyon bayan kokarin da MDD take yi na shiga tsakanin rikicin kasar ta Sham
2014-06-23 20:53:28 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying ta bayyana matsayin da Sin ke dauka kan halin da kasar Sham ke ciki a taron manema labaru da aka saba yi a ran 23 ga wata, inda ta ce, Sin na goyon bayan kokarin da MDD take yi na shiga tsakanin rikicin kasar ta Sham. Ta kara da cewa, ya kamata kasashen duniya su mai da muhimmanci sosai kan yadda ta'addanci da masu tsatsauran ra'ayi ke yaduwa .

Madam Hua ta nuna cewa, Sin na dora muhimmanci sosai kan sa kaimi ga warware rikicin kasar Sham a siyasance, a ganinta, ya kamata a nace ga ka'idoji biyar, wato warware rikicin ta hanyar siyasa, baiwa jama'ar kasar ikon zaben hanyar da kasar za ta bi nan gaba, tsaya wa tsayin daka kan samun sauyi a fannin siyasa ta nuna hakuri ga bangarori daban-daban, sannan da tabbatar da samun sulhuntawa da hadin gwiwar al'umma, da ci gaba da bin hanyar samarwa sauran kasashen dake kewaye da kasar Sham tallafin jin kai. Muhimmin aikin da aka sa gaba shi ne, sa kaimi ga bangarorin biyu a kasar ta Sham da su zabi hanya mai dacewa da za ta kare moriyar bangarori daban-daban. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China