A ran 4 ga wata, kotun kula da tsarin mulki ta koli ta kasar Sham ta sanar da sunayen mutanen da za su shiga takaran babban zaben shugaban kasar a hukunce, wanda a ciki har da shugaba mai ci Bashar al-Assad da wadansu mutane biyu.
Wa'adin aiki na shugaban kasa a Sham ya kai shekaru 7, tun daga shekarar 2000 har zuwa yanzu, Bashar al-Assad ya ke shugabancin kasar da yanzu yake cikin wa'adi na biyu. Wannan zabe ya zama karo na farko da kasar Sham za ta gudanar da irin shi wanda zai fitar da 'yan takara da suka fi mukami yawa. (Danladi)