in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hari da makaman igwa a wurare da dama a kasar Sham
2014-03-19 14:49:45 cri
A ranar Talata 18 ga wata ne, aka kai farmaki da makaman igwa a yankunan karkarar birnin Damascus, da birnin Homs da ke tsakiyar kasar Sham da dai sauransu, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 13 tare da jikkata wasu 52. Kamfanin dillancin labaru na gwamnatin kasar Sham ya bayyana a wannan rana cewa, 'yan adawa da suka ja daga a yankunan da dama na kasar, yanzu sun yi amfani da makaman harba rokoki da boma-bomai don tsoratar da fararen hula.

A wannan rana kuma, sojojin kasar Isra'ila sun tabbatar da cewa, an kai harin bom a yankin Tuddan Golan da ke dab da bakin iyakar Sham da Isra'ila, lamarin da ya raunata sojojin Isra'ila 4. Bayan fashewar bom din, sojojin Isra'ila sun jefa boma-bomai a wasu yankunan kasar Sham.

Tun bayan da aka fara yakin basasa a kasar Sham, ake ta yin musayar wuta da kai hare-hare da boma-bomai a wuraren da ke dab da bakin iyakar Sham da Isra'ila a yankin Tuddan Golan. Bisa labarun da muka samu daga kafofin watsa labaru na Isra'ila, an ce, jiragen saman yaki na Isra'ila sun jefa boma-bomai da yawa a wurare da dama a fadin kasar Sham. (Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China