in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya jaddada wajibcin bunkasa fannin kirkire-kirkiren kasar
2014-06-09 20:36:28 cri
An kira taro karo na 17 na masu zurfin ilmi na cibiyar nazarin kimiyya da fasaha na kasar Sin, da kuma taro na 12 na masu zurfin ilmi na cibiyar nazarin fasahohin masana'antun kasar Sin a yau Litinin 9 ga wata a nan birnin Beijing inda shugaban kasar Sin Mr Xi Jinping ya halarta tare da ba da jawabi. Shugaban ya jaddada wajibcin nacewa ga bin hanyar yin kirkire-kirkire bisa halin da Sin ke ciki, tare da ingiza raya kasa a fannin kirkire-kirkire.

Shugaba Xi Jinping ya kuma nanata cewa, a halin yanzu an kusa cimma muradun da aka tsara na raya al'ummar Sinawa idan aka kwatanta da sauran lokuta a tarihi, hakan ya sa, ana da kwarin gwiwa sosai bisa na sauran lokuta, don haka ake da imanin cewa, za a cimma wannan buri.

A cewar shugaban, domin cimma wannan muradi, kamata ya yi a nace ga tsarin raya kasa ta hanyar koyar da ilmi da fasaha, da kuma gudanar da aikin kirkire-kirkire tare da nacewa ga bin hanyar raya kasa ta yin amfani da kimiyya da fasaha. Ya kamata a yiwa tsarin horaswa kwaskwarima da shigo da masu zurfin ilmi, a kokarin da ake na horar da ilmi mai zurfi a fannin kirkire-kirkiren masana'antu dake sahon gaba a duniya. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China