in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nauyin tsaron kasashen Asiya ya rataya ne a wuyan kasashen yankin, in ji shugaba Xi
2014-05-21 15:12:32 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi kira ga daukacin kasashen Asiya, da su hada kai da juna wajen tabbatar da tsaron yankin yadda ya kamata, aikin da a cewar sa ya rataya kaco-kan a wuyan kasashen dake nahiyar.

Shugaba Xi wanda ya bayyana hakan cikin jawabin sa na bude taron tattaunawa kan inganta cudanya, da karfafa hadin gwiwar nahiyar Asiya na CICA, karo na hudu da aka fara Larabar nan a birnin Shanghai, ya kara da cewa wajibi ne kasashen nahiyar su maida hankali ga batun tsaro ta hanyar hadin gwiwa, tare da daukar matakan magance rikice-rikice ta hanyoyin lumana.

Har ila yau shugaba Xi ya ce lokaci ya wuce da kasashen Asiya za su kafe wajen amfani da tsohon tunani na zaman doya da manja. Don haka ya ce dole ne a yayata bukatar aiwatar da hadin gwiwa, game da wanzar da tsaron nahiyar cikin dogon lokaci.

Shugaban kasar ta Sin wanda ya bayyana taron CICA a matsayin taro mafi girma, da ke bada damar tattauna batutuwan da suka jibanci tsaron shiyyar, ya kara da cewa akwai bukatar fadada hadin gwiwar CICA, da sauran hukumomi da cibiyoyin da ba na gwamnati ba, domin cimma kudurorin taron ta fuskar inganta tsaro.

Bugu da kari shugaban kasar ta Sin ya ce kasar sa za ta sauke nauyin dake wuyan ta na jagorancin taron na bana, ta hanyar yin aiki kafada-da-kafada da sauran kasashen nahiyar, wajen daukaka matsayin harkar tsaron nahiyar zuwa matsayi na gaba. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China