in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe taro karo na biyu na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasar kasar Sin zagaye na 12
2014-03-12 11:02:23 cri
 

An rufe taro karo na biyu, na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasar kasar Sin ko CPPCC zagaye na 12, da safiyar yau Laraba 12 ga wata a babban dakin taron jama'a. Inda taron ya yi kira ga sassan CPPCC, da mahalarta taron, da mambobin majalisar da su kara hada kai karkashin jagorancin shugaban kasar Sin Xi Jinpping, da nacewa ga hanyar raya kasa bisa tsarin musamman na gurguzu, ta yadda za a tabbatar da wadata cikin al'umma da raya al'ummar Sinawa.

Shugaban majalisar ba da shawara ta kasar Sin Mr Yu Zhengsheng, shi ne ya jagoranci bikin rufe taron. Kuma wasu manyan shugabanni sun halarci taron, da suka hada da suhgaba Xi Jinping, da firaministan kasar Li Keqiang, da wasu sauran zaunannun wakilan majalisar siyasa ta kwamitin tsakiyar jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin Zhang Dejiang, da Liu Yunshan, da Wang Qishan,da kuma Zhang Gaoli.

Har ila yau taron ya zartas da kudurin da taro karo na biyu, na CPPCC zagaye na 12 ya gabatar kan ayyukan zaunannen kwamitin, da rahoton da kwamitin ba da shawara ya gabatar, dangane da nazarin da aka yi kan shawarwarin da aka gabatar yayin taron na wannan karo, da kuma kudurin siyasa na taron.

Wakilai da jami'an kwamitin tsakiyar jam'iyyar kwaminis ta Sin, da majalisar gudanarwa sun halarci bikin rufe taron, baya ga jakadun kasashe da dama dake birnin Beijing. (Amina)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China