in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jojin kasar Sin ya bayyana kudurinsa na yaki da ta'addanci a fadin kasar
2014-03-10 20:39:16 cri
Shugaban kotun kolin al'umma na kasar Sin (SPC) Zhou Qiang, ya lashi takwabin aiwatar da hukunci mai tsanani kan laifuffukan da suka shafi ta'addanci a fadin kasar, kamar harin da ya faru a tashar jirgin kasan Kunming.

Mr Zhou ya bayyana hakan ne yayin da yake gabatar da rahoton aikin kotun a cikakken zama na biyu na taron wakilan jama'ar kasar Sin karo na 12 da ke gudana a nan birnin Beijing domin su yi nazari a kai.

Ya ce, daga yanzu kotuna za su yanke hukunci mai tsanani kan wadanda suka aikata laifukan kawo illa ga tsaron kasa, musamman wadanda suka kai hare-hare ta'addanci, kawo barazana ga tsaron lafiyar jama'a da kuma lalata kayayyakin tsaro na soja.

Idan ba a manta ba, a ranar 1 ga watan Maris ne, wasu 'yan ta'adda dauke da wukake suka kashe fararen hula da ba su san hawa ba balle sauka a tashar jirgin kasa da ke Kunming na lardin Yunnan na kasar Sin, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane 29 tare da jikkata wasu 143. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China