Yau Jumma'a 15 ga wata, an kada kuri'a a gun taro na farko na majalisar wakilai na 12 na jama'ar kasar Sin, inda aka tabbatar da cewa, Li Keqiang ya zama firaministan majalisar gudanarwa ta Jamhuriyar Jama'ar kasar Sin.
Kuma Zhou Qiang ya zama shugaban kotun koli ta jama'a. Yayin da Cao Jianming ya zama shugaban hukumar koli ta bin bahasi ta jama'a. (Amina)