in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojin 'yantar da kasar Sham ba zai halarci taron Geneva ba
2013-11-27 17:17:37 cri

Salim Idris, shugaban babbar kungiyar adawa da gwamantin kasar Sham a cikin gida wato sojin 'yantar da kasar Sham ya bayyana a ran 26 ga wata cewa, sojin ba zai shiga taron Geneva ba, ban da haka, zai ci gaba da jan daga da sojin gwamnatin kasar har sai an sauke shugaba Bashar al-Assad daga mukamin sa.

Kafin wannan, babbar kungiyar adawa da gwamnatin kasar Sham a kasashen waje ta kawancen 'yan adawa da masu juyin juya hali ta taba amincewa da shiga taron na Geneva, amma da sharadi.

A ganin wassu manazarta, ko da idan bangarori daban-daban masu halartar taron Geneva sun cimma matsaya daya daga wasu fannoni kan batun kasar Sham, ba za a iya tabbatar da su ba saboda ganin rashin samun goyon baya daga masu dauke da makamai a kasar. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China