in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana hasashen cewa, za a kira taron Geneva karo na biyu kan batun Sham a watan Nuwamba na bana
2013-10-21 10:32:45 cri

Babban satakaren kungiyar tarayyar kasashen Larabawa wato AL Nabil al-Arabi ya bayyana a ran 20 ga wata cewa, ana kyautata zaton cewa, za a shirya taron Geneva karo na biyu kan batun kasar Sham daga ranar 23 zuwa 24 ga watan Nuwamba na bana.

Nabil al-Arabi ya yi wannan bayani ne a ganawar sa da Lakhdar Brahimi,manzon musamman na MDD da AL mai kula da rikicin Sham a cibiyar kungiyar ta AL da ke birnin Alkahira.

A ganawar , sun tattauna kan halin baya-bayan da ake ciki a Sham, da kuma ayyukan da ake gudanarwa wajen warware rikicin siyasa a kasar Sham, domin share fage ga taron Geneva karo na biyu.

Shi kuma Lakhdar Brahimi ya bayanin cewa, 'yan adawa daga kasar Sham za su halarci wannan taron Geneva.(Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China