in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar 'yan adawa da gwamnatin kasar Sham sun yarda da shiga taron Geneva bisa wasu sharudda
2013-11-13 11:00:24 cri
Kungiyar adawa da gwamnatin kasar Sham mafi girma dake wajen kasar, wato Gamayyar kungiyoyin 'yan adawar Syria, ta ba da sanarwa a daren ranar 11 ga wata cewa, ta yarda ta shiga taron da za a yi a Geneva bisa wasu sharudda.

Sanarwar ta nuna cewa, babban sharadin dake sahun gaba shi ne, shugaba Bashar Al-Asaad ya yi murabas daga mukaminsa, kuma a haramtawa shugaban da magoyansa samun ko wace irin kujerar wakilci a gwamnatin wuci gadi, da ma gwamnatin da za a kafa a nan gaba.

Ban da haka, sanarwar ta nemi kasashen duniya da su samar da wata hanya a cikin kasar ta Sham, wadda za a yi amfani da ita wajen samar da kayayyakin jin kai, tare kuma da yin kira ga gwamnatin kasar da ta saki mutane da ake tsare da su bisa laifuffukan siyasa.

Ya zuwa yanzu, gwamnatin Syria ta riga ta bayyana matsayinta na shiga taron, amma ta ki yarda da zama teburin shawarwari da wadanda ta kira 'yan ta'adda. Har ila yau gwamnatin ta ki amincewa da kasashen waje su sanya baki cikin tattaunawar da za a yi.

A hannu guda kuma, ragowar kungiyoyin adawar ba su cimma matsaya daya ba kan ko za su shiga taron ko kuwa a'a. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China