in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen duniya na mai da muhimmanci sosai kan labarin yin amfani da makamai masu guba na kasar Sham
2013-08-23 16:01:20 cri
Yanzu rukuni mai binciken makamai masu guba a kasar Sham na MDD yana gudanar da aikinsa a kasar, domin nazari kan labarin da aka bayar na cewa, akwai yiwuwar yin amfani da makamai masu guba a wasu wurare uku ciki hadda garin Khan al-Assal na lardin Aleppo. Amma, a ran 21 ga wata, an sake samu irin wannan labari cewa, an yi amfani da makamai masu guba cikin wata fafatawar da ta wakana tsakanin sojojin kasar da masu adawa da gwamnati, bangarorin biyu na zargin juna game da amfani da makamai masu guba, abin da ya yi sanadin asarar rayuka sama da dubu, lamarin da ya jawo hankalin kasa da kasa.

Kwamitin sulhu na MDD ya kira wani taro cikin gaggawa a wannan rana domin tattauna kan batun, kuma babban sakatare Ban Ki-Moon ya ba da sanarwa ta bakin kakakinsa a ran 22 ga wata, inda ya nanata wajibacin nazari kan wannan batu cikin sauri, kuma ya ce, ya tura jami'an MDD zuwa kasar Sham.

Kakakiyar ma'aikatar harkokin waje ta kasar Amurka Madam Jen Psaki ta bayyana a ran 22 ga wata cewa, gwamnatin kasar tana hadin gwiwa da kawayenta da wasu kasashen yankin gabas ta tsakiya domin dudduba kan lamarin tun da wuri. Kakakin ma'aikatar harkokin waje na kasar Rasha Alexander Lukashevich ya bayyana a ran 22 ga wata cewa, matsayin da kasar za ta dauka kan wannan lamari ya dogaro da binciken da MDD take yi. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China