in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana ci gaba da aikin lalata makamai masu guba a kasar Sham
2013-10-08 16:40:40 cri
Rukunin share fage na tawagar kwararru da ke binciken makamai masu guba daga hukumar haramta makamai masu guba ta duniya yana ci gaba da aikin lalata makamai masu guaba a kasar Sham, tawagar kwararrun ta bayyana cewa, gwamnatin kasar Sham tana maraba da aikin da tawagar ke gudanarwa.

Kwararru sun shiga cikin wa'adi na biyu na aikinsu da ya shafi aikin yin bincike da kuma kwance makamai masu guba, har ma da lalata su.

Ta wani bangare, kamfanin dillancin labaru na Sham ya bayar da wani labari cewa, a ran nan, sojojin gwamnati sun kai samame tare raunana wasu mayakan kungiyar 'Jabhat al-Nusra Front' a yankunan Al-kabon da Jobar da dai sauransu, tare da lalata makamansu.

Ahmad al-Jarba, shugaban kungiyar dake adawa da gwamnatin Assad da ke wajen kasar Sham, ya bayyana a ran 7 ga wata cewa, 'yan adawa sun yarda da halartar taron duniya na biyu da za a gudana a birnin Geneva kan batun Sham. A sa'i daya kuma, Ahmad al-Jarba ya ce, sam 'yan adawa ba za su yi shawarwari da gwamnatin Bashar al-Assad ba, sun bukaci da ya sauka daga mukaminsa. (Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China