in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin waje na Amurka da Rasha sun yi shawarwari yayin taron koli na APEC
2013-10-07 16:48:19 cri
Sakataren harkokin waje na kasar Amurka John Kerry da ministan harkokin waje na kasar Rasha Sergei Lavrov sun yi shawarwari yayin taron koli na APEC a ranar 7 ga wata, sannan suka gana da manema labaru tare. A ganawar, Mr Kerry ya bayyana cewa, idan gwamnatin kasar Syria ta bi kudurin MDD na lalata makamai masu guba na kasar, watakila za ta sake samu goyon baya daga kasa da kasa. Shi ma Mr Lavrov a bayaninsa ya ce, kasarsa za ta tabbatar da gwamnatin kasar Syria ta yi hadin gwiwa tare da rukunin kwararru na MDD da hukumar hana amfani da makamai masu guba wato OPCW wajen gudanar da ayyukansu a kasar.

Rukunin kwararru na MDD da hukumar OPCW ya fara gudanar da aikin kawar da dakunan ajiye makamai masu guba a kasar Syria. Dangane da haka, Mr Kerry ya bayyana cewa, wannan aiki na da muhimmanci sosai wajen warware batun makamai masu guba na kasar Syria. Wannan wani mafari ne mai kyau. Kuma kasar Amurka tana maraba da shi.

Haka kuma jami'an biyu sun bayyana cewa, za su yi shawarwari tare da wakilin musamman na MDD da kungiyar kawancen kasashen Larabawa Lakhdar Brahimi, da yin kokari wajen gduanar da taron kasa da kasa na biyu kan batun kasar Syria a tsakiyar watan Nuwamba na bana.

Ban da wannan kuma, Kerry da Lavrov sun tattauna kan batun nukiliya na kasar Iran. Inda bangarorin biyu suka nuna fatan za a samu kyakkyawan sakamako a shawarwari a tsakanin bangarori shida wato Amurka, Ingila, Faransa, Rasha, Sin da Jamus, da kungiyar EU, da kuma kasar Iran a birnin Geneve dake kasar Switzerland a ranar 15 ga wata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China