in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a dakatar da musayar wuta don tabbatar da aikin ceto a Syria
2013-10-20 17:15:35 cri
Ran 19 ga wata, mataimakiyar babban sakataren kula da harkokin jin kai ta MDD Valerie Amos ta ba da wata sanarwa inda ta nuna matukar damuwarta kan halin jin kai da kasar Syria ke ciki a halin yanzu, kuma ta yi kira ga bangarori daban daban na kasar da su dakatar da musayar wuta da ke tsakaninsu don tabbatar da tsaron jama'ar kasar da kuma gudanar da ayyukan agaji.

Valerie Amos ta bayyana cewa, a duk fadin kasar, jama'ar Syria suna fuskantar tashin hankali, kullum tana damuwa kan lamarin, kuma cikin watanni da dama da suka gabata, ba a samu ci gaba ko kadan ba kan aikin ba da agaji a wani garin da ke yankin karkarar babban birnin kasar, Damascus. Ko da yake mutane kimanin dubu 3 sun janye daga wurin, amma akwai mutane da dama ba su fita daga yankin ba.

Don haka, Valerie Amos ta yi kira ga bangarori daban daban da su cimma ra'ayi daya kan dakatar da musayar wuta a yankin, ta yadda hukumomin ba da taimakon jin kai za su iya shiga yankin don samar da ayyukan ceto. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China