in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira ga sassa daban daban na Sham da su warware rikici ta hanyar yin tattaunawa
2013-09-30 20:39:30 cri
Ranar Litinin 30 ga wata, Hong Lei, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing cewa, kasar Sin ta yi kira ga sassa daban daban na kasar Syria masu ruwa da tsaki da su tsagaita bude wuta cikin hanzari, a kokarin warware rikicin kasar ta hanyar yin tattaunawa.

Hong Lei ya kara da cewa, kullum kasar Sin na ganin cewa, warware batun Syria a siyasance, ita ce hanya daya kacal da za a iya bi. Don haka kasar Sin za ta ci gaba da yin iyakacin kokarinta tare da sauran kasashen duniya wajen aiwatar da kudurori da shawarwarin da abin ya shafa, a kokarin ba da gudummowa a fannin warware batun na Syria yadda ya kamata daga dukkan fannoni kuma cikin dogon lokaci.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China