in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Iran ta karbi ikon mallakar wata tashar samar da wutar lantarki daga kasar Rasha
2013-09-24 16:03:03 cri

An yi bikin mika ikon mallakar tashar samar da wutar lantarki mai amfani da makamashin nukiliya, tsakanin jami'an kasar Iran da na kasar Rasha a ranar Litinin 23 ga watan nan, a birnin Bushehr dake kudancin kasar Iran. Matakin da ya baiwa kasar ta Iran cikakken ikon mallakar wannan tasha a hukunce, kuma za ta kasance irinta ta farko a kasar.

Hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa (IAEA), ta shafe tsahon shekaru tana sa ido kan harkokin wannan tasha, don haka, ba a shakkun ayyukan da tashar ke gudanarwa ta fannin biyan bukatun fararen hula. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China