in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata jami'ar kungiyar EU ta yi kira ga Iran da ta gaggauta yin shawarwari kan batun nukiliya
2013-08-07 14:59:27 cri
A ranar 6 ga wata, wakiliyar kungiyar EU game da harkokin diplomasiyya da tsaro Catherine Ashton ta yi kira ga sabon shugaban kasar Iran Hassan Rouhani da ya gaggauta yin shawarwari na sabon zageye da kasashe 6 da abin ya shafa game da batun nukiliya na kasar.

Bisa labarin da kafofin yada labaru na wurin suka bayar, an ce, Ashton ta aika da sako ga Hassan Rouhani don taya shi murnar zama shugaban kasar, kuma ta ce, ya samu cikakken goyon baya, kuma zai iya yin shawarwari da hadin gwiwa da kasashen duniya, don gaggauta warware shirin nukiliya na kasar Iran.

A cikin wasikar, Ashton ta ce, a shirye take don ci gaba da yin shawarwari, kuma tana fatan gaggauta shirya taron tattaunawa mai ma'ana da rukunin shawarwari na kasar Iran.

A ranar 4 ga wata, Rouhani ya yi rantsuwar kaman aiki, a matsayin shugaban kasar Iran na 11. A ranar 6 ga wata, a birnin Tehren Rouhani ya bayyana cewa, Iran tana fatan gaggauta farfado da shawarwari kan batun nukiliya na kasar cikin tsanaki. Amma ya jaddada cewa, tace sinadarin uranium hakkin kasar Iran ne, Iran ba za ta daina wannan aiki ba, kuma Rouhani ya ce, ba zai kawar da yiwuwar yin shawarwari kai tsaye da kasar Amurka ba.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China