in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ta yi shirin mayar da martani game da batun nukiliya
2013-09-13 15:40:51 cri
A ranar 12 ga wata, sabon wakilin kasar Iran a hukumar makamashi ta duniya wato IAEA Reza Najafi ya bayyana cewa, Iran a shirye take don mayar da martani game da shakku da ake nunawa game da batun nukiliya da kuma hadin gwiwa da ke tsakaninta da hukumar IAEA, amma a sa'i daya kuma, ya jaddada cewa, ba zai yi sassauci game da hakkin raya nukiliya na kasar ba.

A wannan rana, Najafi ya yi bayani game da batun nukiliya na kasar Iran karo na farko a gun taron kwamitin hukumar IAEA, inda ya ce, a karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya, Iran za ta sauke nauyin da ke wuyanta, da bayyana shakkun da aka nuna mata game da batun nukiliya, kuma za ta hada gwiwa da hukumar IAEA cikin sahikanci don daddale shirin kafa tsarin yin bincike.

Wakilinn kasar ta Iran a sa'i daya kuma, ya jaddada cewa, kasar sa zata raya shirin nukiliya domin zaman lafiya, kuma bisa yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya, yace Iran tana da hakkin raya nukiliya don zaman lafiya, kuma ba zai yi sassauci game da wannan batu ba.

Najafi ya kuma bayyana cewa, Iran a shirye take, don tsara wani shirin yin shawarwari game da batun nukiliya na kasar cikin dogon lokaci, bisa tushen girmama juna da moriyar juna, amma ya bukaci bangarorin da abin ya shafa da su daina kawo kalubale ko saka takunkumi, sannan su girmama kasar Iran yadda ya kamata.

A gun taron kwamitin da aka yi a ran nan, wakilin kasar Amurka a hukumar IAEA Joseph E. Macmanus ya ce, kasar Iran ta yi amfani da shirin kafa wani tsari don kawo jinkiri game da aikin bincike, kuma ya bukaci Iran da ta daina yin wasan dabarun jinkiri, ta hadin gwiwa da hukumar IAEA daga duk fannoni, ta kuma amince da binciken da za a yi mata.

A sa'i daya kuma, Joseph E. Macmanus ya jaddada cewa, idan ba a samu takamaiman ci gaba ba a gun taron kwamiti na karo mai zuwa, Amurka da sauran mambobin kwamitin za su dauki tsattsauran matakan diplomasiyya don yin matsin lamba ga kasar Iran.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China